An sauya sunan jami’ar Abuja zuwa Yakubu Gowon University

Gwamnatin Tarayya ta sauya sunan Jami’ar Abuja zuwa Yakubu Gowon University.
Gwamnatin Tarayya ta sanar da sauya sunan Jami’ar Abuja (UniAbuja) zuwa Jami’ar Yakubu Gowon.
Ministan Labarai, Mohammed Idris, ya bayyana haka ga manema labarai na fadar shugaban kasa a ranar Litinin, bayan zaman majalisar zartarwa ta tarayya (FEC) wanda shugaban kasa Bola Tinubu ya jagoranta.
Yace canjin sunan na nufin girmamawa ga tsohon shugaban kasa, Janar Yakubu Gowon (mai ritaya), wanda ya cika shekaru 90 kwanan nan.
Idris ya bayyana cewa za a gabatar da kudurin sauya sunan ga majalisar dokoki ta Kasa domin samun amincewar ta.
An sauya sunan jami’ar Abuja zuwa Yakubu Gowon University


Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe to get the latest posts sent to your email.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe now to keep reading and get access to the full archive.

Continue reading