Kungiyar gwamnoni tayi alhini kan rasuwar Yarima Abdulkadir Mahe

Kungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ta bayyana alhini kan rasuwar Yarima Abdulkadir Mahe, shugaban ma’aikatan gidan gwamnatin Jihar Kwara kuma na hannun damar shugaban NGF, Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq.
A wata sanarwa da babban darakta na NGF, Dakta L.O.T. Shittu ya fitar, kungiyar ta bayyana Yarima Mahe a matsayin jajirtaccen ma’aikacin gwamnati wanda ya bayar da muhimmiyar gudunmawa wajen cigaban Jihar Kwara da Najeriya baki ɗaya.
NGF ta ce marigayin ya kasance mutum mai nagarta wanda ya jajirce wajen tabbatar da kyakkyawan shugabanci.
Sanarwar ta kuma isar da ta’aziyya ga Gwamna Abdulrazaq, gwamnatin Jihar Kwara, al’ummar jihar, da iyalan mamacin, tana mai addu’ar Allah ya jikansa da rahama ya kuma sanya shi cikin Aljannatul Firdausi.
Kungiyar gwamnoni tayi alhini kan rasuwar Yarima Abdulkadir Mahe


Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe to get the latest posts sent to your email.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe now to keep reading and get access to the full archive.

Continue reading