Mataimakin shugaban kasa, Shettima ya bar Dubai zuwa Saudiyya

Mataimakin S’dhugaban kasa, Kashim Shettima, ya bar Dubai zuwa Saudi Arabia bayan ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bude wata cibiyar samar da man fetur da ajiya mai darajar Dala miliyan 315.
Bayan taron na Dubai, mataimakin shugaban kasa zai ci gaba da gudanar da Umrah a biranen Madinah da Makkah daga ranar 16 zuwa 19 ga Disamba, 2024.
A tare da Kashim Shettima akwai gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum.
A ranar 20 ga Disamba, 2024, Shettima zai yi wata ganawa ta musamman da shugaban bankin raya kasashen musulunci (IsDB) a birnin Jeddah.
Tattaunawar za ta mayar da hankali kan shirin haɗin gwiwar kuɗaɗe don kananan yankunan sarrafa kayayyakin noma na II da kuma inganta hadin kai a ayyukan IsDB a Najeriya don tallafa wa ci gaban tattalin arziki da aikin noma na ƙasar.
Mataimakin shugaban kasa, Shettima ya bar Dubai zuwa Saudiyya


Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe to get the latest posts sent to your email.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe now to keep reading and get access to the full archive.

Continue reading