Rundunar yan sanda ta kama dan fashi da makami a Bauchi

Yan sanda a jihar Bauchi sun kama wani Suleiman Adamu, mai shekaru 40, a unguwar Sabon Layi, bisa zargin satar motoci da fashi da makami.
An kama shi ne yayin wani samame da rundunar ta gudanar, yayin farmakin an samu bindiga, harsasai.
Bugu da ƙari, an gano lambar lasisin motoci guda biyu a hannun wanda ake zargin.
Kakakin rundunar Ahmed Wakili yace binciken da suka gudanar ya kai ga kama wani mai suna Adamu Sale, mai shekaru 30 a unguwar Rafin Makaranta. Wanda ake alkanatawa da jerin sace sacen motoci a garin Zaranda, cikin ƙaramar Hukumar Toro.
Masu laifin sun amsa laifinsu, suna bayyana cewa suna amfani da bindigar hannu ne wajen aikata laifin.
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, CP Auwal Musa Mohammed, ya umurci a ci gaba da bincike mai zurfi don gano sauran mambobin kungiyar da kuma dawo da sauran motocin da aka
sace
Rundunar yan sanda ta kama dan fashi da makami a Bauchi


Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe to get the latest posts sent to your email.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe now to keep reading and get access to the full archive.

Continue reading