Tinubu yayi alhinin rasuwar tsohon Alkalin Kotun Koli, Uthman Argungu

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya bayyana jimamin sa kan rasuwar Justice Uthman Argungu, wanda yayi ritaya daga aikin kotun koli ta Najeriya.
Justice Argungu, wanda ya rasu yana da shekara 90, an binne shi ranar Lahadi a garinsa, Argungu, a Jihar Kebbi, bisa tsarin Musulunci.
A cikin wata sanarwa mai cike da tausayi, da Bayo Onanuga, Mai Ba da Shawara na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Bayani da Tsare-tsare, ya fitar, Shugaba Tinubu ya tuna da tsohon alkalin ne a matsayin wani babban lauya wanda gudummawar sa ga shari’a da aikin lauya ba za ta taɓa misaltuwa ba.
“Justice Argungu ya rayu cikin rayuwa ta sadaukarwa ga ɗan adam da kuma hidima ga ƙasarsa tare da gaskiya da himma da ba za a iya misalta su ba,” in ji Tinubu.
A cikin girmamawa ga gudummawar da ya bayar, Tinubu ya yi addu’a don samun rahama ga ruhin mamacin, sannan ya mika ta’aziyyarsa ga iyalansa, gwamnatin Kebbi da kuma al’ummar jihar.
Tinubu yayi alhinin rasuwar tsohon Alkalin Kotun Koli, Uthman Argungu


Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe to get the latest posts sent to your email.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe now to keep reading and get access to the full archive.

Continue reading