Yan sanda sun kama gungun masu aikata laifi a Yobe

Rundunar ‘yan sandan Yobe ta kama wasu mutane da ake zargi da barayi ne dauke da katunan ATM guda 47, wayoyin salula guda hudu, da wata mota kirar Mercedes Benz.
Mutum shida da lamarin ya rutsa da su
ciki har da mai nakasar gani da ya yi asarar N181,550, sun tabbatar da mutanen da ake zargin tabbas sune sukayi musu satar.
Kwamishinan ‘yan sanda, CP Garba Ahmed, ya umurci ‘yan sanda da su kara tsananta bincike tare da bin diddigin ‘yan kungiyar da suka tsere.
Ya kuma bukaci jama’a da su kai rahoton duk wani abu da ake zargi, ya kuma yi gargadin cewa jihar Yobe ba za ta zama mafakar masu aikata laifuka ba.
Yan sanda sun kama gungun masu aikata laifi a Yobe


Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe to get the latest posts sent to your email.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Discover more from viewnowafrica.com.ng

Subscribe now to keep reading and get access to the full archive.

Continue reading